DCL Hausa Radio
Kaitsaye

ADC ta nesanta kanta da Nasiru El-Rufa’i bayan taron jam’iyyar da aka yi tashin hankali a Kaduna

-

Rikicin siyasa na ƙara kamari a jihar Kaduna bayan jam’iyyar ADC ta nesanta kanta daga wani taron da aka danganta da tsohon gwamnan jihar, Nasir El-Rufa’i, a daidai lokacin da rundunar ‘yan sanda ta fara bincike kan zarge-zargen tashin hankali da harbe-harbe a wajen taron.

A wata sanarwa da mai magana da yawun ADC na jihar Kaduna, Injiniya Musa Idris, ya sanya wa hannu a ranar Asabar, jam’iyyar ta karyata abin da aka kira kwamitin wadanda suka sauya sheka daga APC, PDP, SDP, LP, NNPP zuwa ADC, da aka ƙaddamarwa.

Jam’iyyar ta jaddada cewa El-Rufa’i ba ɗan ADC bane, don haka bai da wani hurumin shirya taruka a madadinta.

A gefe guda kuma, rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna ta tabbatar da cewa ta fara binciken lamarin bayan samun rahoton cewa ‘yan daba sun yi ɓarna a wajen taron siyasar.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara