DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Dokar ta-bacin da aka kakaba a jihar Rivers za ta kare a ranar 18 ga watan Satumba, 2025, in ji Nyesom Wike

-

Ministan Abuja Nyesom Wike, ya bayyana kwarin gwiwar cewa dokar ta-baci da aka ayyana a jihar Rivers za ta ƙare aiki a ranar 18 ga Satumba.

Wike ya bayyana hakan ne bayan ya kada kuri’arsa a zaben kananan hukumomi da ke gudana a jihar.

Ya ce ƙarewar dokar ta-bacin zai bai wa majalisar dokokin jihar damar ci gaba da gudanar da harkokinta na majalisa.

Ministan ya kuma bayyana cewa yanayi ya nuna dacewar cire dokar ta-bacin tun da gwamnati ta jiha da ta kananan hukumomi dukkansu suna da wakilci yanzu.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara