DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jam‘iyyar APC ta lashe kujeru 20 cikin 23 a zaben kananan hukumomin jihar Rivers

-

Jam’iyyar APC ta lashe kujerun shugabannin kananan hukumomi da kansiloli a kananan hukumomi 20 daga cikin 23 da aka gudanar a ranar Asabar.

Ita kuwa jam’iyyar da ke mulki a jihar wato PDP, ta samu nasara a kananan hukumomi uku kacal a zaɓen da hukumar zaɓen mai zaman kanta ta jihar Rivers (RSIEC) ta gudanar.

Gwamna Siminalayi Fubara ma ya sha kaye a mazabarsa ta karamar hukumar Opobo-Nkoro inda babbar jam’iyyar adawa ta jihar ta yi nasara.

Shugaban RSIEC, Dr. Michael Odey, ne ya bayyana sakamakon a ofishin hukumar da ke kan titin Aba Road a birnin Fatakwal, a ranar Lahadi da rana.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara