DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Fa’iza Abdulkadir, mai aikin shara da goge-goge da ta mayar da Naira miliyan 4.8 ta samu kyautar miliyan 2.5

-

Matar da ke aikin shara da goge-goge a asibitin koyarwa na jami’ar Maiduguri Faiza Abdulkadir, wadda ta mayar da naira miliyan 4.8 da aka tura mata a asusun bankinta bisa kuskure, ta samu kyautar naira miliyan 2.5 daga wani mutum da ba a bayyana sunansa ba.

An mika mata wannan tallafi ne a ranar Litinin a Maiduguri ta hannun shugabar ƙungiyar Da’awah Wal Irshaad Women Organisation ta jihar Borno, Hajiya Aisha Muhammad Aisami, wadda ta ce mutumin ya karanta labarin matar ne a jaridar Daily Trust sannan ya bukaci a nemo ta domin a karfafa mata gwiwa.

Google search engine

A matsayin ta na ma’aikaciyar asibitin, Fa’iza na samun albashin N30,000 kacal a kowane wata, tana kuma daukar nauyin mahaifiyarta da kuma ‘ya’yanta guda biyar.

Tun da fari matar gwamnan jihar Borno, Dr Falmata Babagana Zulum, ta yi mata kyautar Naira miliyan guda tare da kayan abinci da kayan koyon sana’o’in dogaro da kai.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara