DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tinubu ya umurci a kai karin kayan yaƙi don magance matsalar tsaro a Katsina

-

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya bayyana shirinsa na tura sabbin kayan yaƙi na zamani da amfani da fasaha zuwa jihar Katsina domin kawo karshen matsalar da ke addabar jihar.

Tinubu ya sanar da hakan ne lokacin da ya karɓi tawagar ’yan jihar karkashin jagorancin Gwamna Dikko Umaru Radda a fadar sa da ke Abuja.

Google search engine

Ya ce wajibi ne a shawo kan kalubalen yana mai umartar hukumomin tsaro su ƙara himma tare da samar da karin jiragen leƙen asiri domin yaki da ‘yan ta’addan.

Shugaban ya kuma bayyana cewa daga yanzu yana buƙatar samun rahoton ayyukan soji a Katsina kullum, tare da jaddada cewa gwamnati ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen kare rayuka da dukiyoyin ’yan Najeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara