DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Nijeriya ta ayyana Juma’a 5 ga watan Satumba a matsayin ranar hutun Maulidi

-

Gwamnatin tarayyar Nijeriya ta ayyana ranar Juma’a, 5 ga Satumban 2025 a matsayin ranar hutu domin bikin Maulidi, wato ranar tunawa da haihuwar Manzon Allah, Annabi Muhammad (SAW).

Ministan harkokin cikin gida, Dr. Olubunmi Tunji-Ojo ne ya sanar da hakan a madadin gwamnatin cikin wata sanarwa da sakatariyar ma’aikatar, Dr. Magdalene Ajani ta fitar.

Google search engine

Tunji-Ojo ya taya al’ummar Musulmi a Nijeriya da ma duniya murna, inda ya yi kira da su yi koyi da kyawawan halayen Annabi (SAW) na zaman lafiya, ƙauna, tawali’u, haƙuri da jin ƙai.

Haka kuma, ministan ya bukaci ’yan Nijeriya masu bin addinai daban-daban da su yi amfani da wannan dama wajen roƙon Allah domin samun zaman lafiya, tsaro da kwanciyar hankali, tare da mara wa gwamnati baya wajen tabbatar da haɗin kai da ci gaban kasar baki daya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara