DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Zan iya kawo karshen ayyukan ‘yan bindiga cikin watanni biyu muddin na samu iko da hukumomin tsaro – Gwamnan Zamfara

-

Gwamnan Zamfara, Dauda Lawal, ya bayyana cewa matsalar ayyukan ’yan bindiga da ke addabar jihar za ta zama tarihi muddin ya samu damar bayar da umarni kai tsaye ga jami’an tsaro.

A cewar gwamnan, yana da cikakkiyar masaniya kan duk inda manyan shugabannin ’yan bindiga suke a jihar, saboda gwamnati tana bibiyarsu a wurare daban-daban na jihar.

Google search engine

Ya ce duk da wannan, rashin ikon da yake da shi na umartar jami’an tsaro ya hana daukar matakin da ya dace a kansu, amma da zai samu wannan ikon cikin watanni biyu za a gama da su.

Gwamnan ya bayyana cewa gwamnatin sa ta dauki matakai masu yawa wajen tallafawa jami’an tsaro da kayan aiki, ciki har da raba motoci 150, daukar dubban jami’an sa kai na CPG, da kuma shigo da mafarauta fiye da 2,000 daga jihohin Borno da Yobe domin taimaka musu wajen yaki da ‘yan ta’addan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara