Ma’aikatar ilimi ta Najeriya ta bayyana cewa Minista Tunji Alausa ne ya ba ƴan matan Yobe da suka lashe gasar Turanci kyautar ₦200,000, ba gwamnatin tarayya ba.
Wata sanarwa da ma’aikatar ta fitar ce ta jaddada hakan, inda ta ce ministan ya bayar da kyautar ne kawai don karfafa gwiwar sauran dalibai wajen mayar da hankali kan karatu.
Sanarwar da aka fitar a ranar 3 ga watan Satumban 2025, ta kuma ce ba a ware wa ma’aikatar wani kasafi don bayar da kyautar ga kowane dalibi a Najeriya ba.
A ranar 28 ga watan Agustan 2025 ne dai aka gabatar da bikin jinjinawa daliban da suka samu nasara a gasar TeenEagle da ta gudanar a kasar Birtaniya.


