DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ba gwamnatin Nijeriya ta ba ƴan matan da suka lashe gasar Turanci kyautar ₦200,000 ba

-

Ma’aikatar ilimi ta Najeriya ta bayyana cewa Minista Tunji Alausa ne ya ba ƴan matan Yobe da suka lashe gasar Turanci kyautar ₦200,000, ba gwamnatin tarayya ba.

Wata sanarwa da ma’aikatar ta fitar ce ta jaddada hakan, inda ta ce ministan ya bayar da kyautar ne kawai don karfafa gwiwar sauran dalibai wajen mayar da hankali kan karatu.

Sanarwar da aka fitar a ranar 3 ga watan Satumban 2025, ta kuma ce ba a ware wa ma’aikatar wani kasafi don bayar da kyautar ga kowane dalibi a Najeriya ba.

A ranar 28 ga watan Agustan 2025 ne dai aka gabatar da bikin jinjinawa daliban da suka samu nasara a gasar TeenEagle da ta gudanar a kasar Birtaniya.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara