DCL Hausa Radio
Kaitsaye

INEC ta fitar da sunan ƙungiyoyi 14 da suka tsallake matakin farko na rajistar jam’iyyu

-

Hukumar zaɓe ta Nijeriya INEC ta bayyana cewa ƙungiyoyi 14 ne kawai daga cikin ƙungiyoyi 171 da suka nemi rajista suka cika sharuddan farko na zama jam’iyyun siyasa.

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Sam Olumekun, kwamishinan hukumar na ƙasa kuma Shugaban Kwamitin Bayanai da wayar da masu zaɓe ya fitar a yau, Alhamis 11 ga Satumba, 2025.

Google search engine

INEC ta ce an tantance buƙatun ne bisa tanade-tanaden Sashe na 222 na Kundin Tsarin Mulki na 1999 (wanda aka yi wa gyara), da Sashe na 79 na Dokar Zaɓe ta 2022, tare da Ka’idojin INEC na 2022.

Hukumar ta bayyana cewa ta wallafa sunayen ƙungiyoyi 14 da suka tsallake wannan mataki a shafinta na yanar gizo da sauran dandamalin ta na hukuma domin jama’a su gani.

INEC ta kuma jaddada cewa rajistar jam’iyyun siyasa aiki ne da zai ci gaba a ƙarƙashin doka, kuma tana bude ƙofa ga kowacce ƙungiya da ta cika sharuddan doka.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara