DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Malami ya kai ƙara ga manyan jami’an tsaro kan zargin shigo da ’yan daba jihar Kebbi

-

Tsohon Attorney janar kuma ministan Shari’a na tarayya, Abubakar Malami (SAN, CON), wanda kuma shi ne jagoran jam’iyyar ADC a Jihar Kebbi, ya rubuta ƙorafi ga mai ba shugaban ƙasa shawara kan tsaro (NSA), shugabannin DSS, ’Yan Sanda, Hukumar Shige da Fice, da Civil Defence domin nuna bukatar gaggawar da lamarin ke da shi.

A cewar ƙorafin, wanda aka sanya wa kwanan watan ranar 10 ga Satumba, 2025, Malami ya yi zargin cewa wasu ’yan siyasa suna haɗin gwiwa da ’yan banga daga Jamhuriyar Nijar tare da basu makamai ta haramtattun hanyoyi.

Google search engine

Ya bayyana cewa ana ‘yan siyasar na shirin tura batagarin domin kai wa jama’a hari, hana ‘yan adawa sakat, da kuma lalata zaman lafiya a jihar.

Malami ya roƙi NSA da sauran shugabannin tsaro da su ɗauki matakan gaggawa ta hanyar haɗa kai tsakanin hukumomin tsaro, tsare iyakokin ƙauyuka don hana shigar ’yan banga da makamai, tare da kaddamar da bincike na musamman kan zargin haɗin guiwar wasu jami’an gwamnati da ’yan ta’adda.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara