DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sojoji sun yi nasarar ceto mutane da kwato Naira miliyan 23 a Sokoto da Zamfara

-

Rundunar Operation Fansar Yamma sun samu nasarori a jerin hare-hare da suka kai a jihohin Zamfara da Sokoto tsakanin 8 zuwa 10 ga watan Satumba, inda suka kwato makudan kudade, dabbobi tare da ceto mutane daga hannun ’yan bindiga.

A cikin wata sanarwa da jami’in yada labarai na rundunar, Kyaftin David Adewusi ya fitar, ya ce dakarun sun kai farmaki a kananan hukumomin Shinkafi, Gusau, Bukkuyum da Tureta, inda suka lalata maboyar ’yan ta’adda tare da fatattakar su.

Google search engine

Ya bayyana cewa an samu nasarar kwato sama da Naira miliyan 23 da ake zargin kudin fansa ne, an kuma ceto wasu daga cikin mutanen da aka sace tare da kwato sama da dabbobi 160 da aka sace.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara