DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sojoji sun hallaka wani kwamandan ‘yan bindiga a jihar Kogi

-

Dakarun rundunar sojin Najeriya ta 12 Brigade, karkashin Operation Accord III, tare da haɗin gwiwar sauran jami’an tsaro, sun yi nasarar halaka wani kwamandan ‘yan bindiga mai suna Babangida Kachala, wanda shi ne mataimakin shugaban dabar da Kachala Shuaibu ke jagoranta a dajin Masalaci Boka da Ofere, Jihar Kogi.

Wannan nasarar ta zo ne mako guda kacal bayan da sojoji suka yi nasarar kashe wani babban kwamandan dabar, Kachalla Balla, tare da wasu ƴan bindiga biyar.

Haka kuma, dakarun tare da tallafin jiragen sama sun gudanar da wasu hare-haren share fagen da ya kai ga ceto fursunonin da aka sace.

Mai magana da yawun rundunar, Lieutenant Hassan Abdullahi, wanda shi ne mukaddashin daraktan hulɗa da jama’a na 12 Brigade, ya tabbatar da wannan nasara a cikin wata sanarwa da aka fitar daga Lokoja a ranar Asabar.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon Minista Tanimu Turaki ya zama ɗan takarar shugabancin jam’iyyar PDP na Arewa

Jagororin jam’iyyar PDP na yankin Arewacin Nijeriya sun amince da tsohon Ministan Harkoki. A Musamman, Tanimu Turaki (SAN), a matsayin ɗan takarar da suka amince...

Jam’iyyar ADC a Kaduna ta kori mataimakin shugabanta da wasu ‘ya’yanta 8

Jam'iyyar hadaka ta ADC mai hamayya a Nijeriya reshen Kaduna ta kori mataimakin shugabanta na jihar tare da wasu manyan jami'anta guda takwas, bayan samun...

Mafi Shahara