Mai Martaba Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, ya ce Nijeriya ba ta yi sa’ar samun shugabanni nagari ba na dogon lokaci.
Ya ce ƙasar tana ta fuskantar shugabannin da ya bayyana a matsayin marasa kwarewa tsawon shekaru da dama.
Sai dai, Sarkin ya ce, da gwamnatin tarayya ba ta cire tallafin mai ba, da ƙasar ta riga da ta durkushe ta fuskar tattalin arziki.



