DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan bindiga sun yi awon gaba da masallata da dama a jihar Zamfara

-

Akalla mutane 40 ne ake zargin ’yan bindiga sun sace da Asuba a wani masallaci da ke kauyen Gidan Turbe, ƙaramar hukumar Tsafe, jihar Zamfara.

Lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 5:30 na asubar ranar Litinin yayin da suke tsaka da sallah.

Google search engine

Wannan harin ya nuna rushewar yarjejeniyar sulhu da aka kulla a watan da ya gabata tsakanin shugabannin al’umma da wasu daga cikin ’yan bindiga a Katsina da Zamfara.

Yarjejeniyar dai ta yi alƙawarin kawo ƙarshen hare-hare da garkuwa da mutane, tare da ba manoma damar yin noma a gonakinsu cikin kwanciyar hankali.

Sai dai kwatsam, wasu daga cikin ’yan bindigar sun ci gaba da kai hare-hare a jihohin arewa maso yamma.

Daily Trust ta rawaito cewa rahotanni sun tabbatar da dakarun Operation fansar yamma na ci gaba da sintiri da kai samame a yankunan da abin ya shafa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara