DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Buba Galadima ya zargi Tinubu da shirya makarkashiya a shugabancin INEC

-

Jigo a jam’iyyar NNPP, Buba Galadima, ya yi ikirarin cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu na shirin naɗa wani tsohon alkalin kotun daukaka ƙara a matsayin sabon shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa INEC.

Da yake magana a wani shiri da gidan talabijin na Arise, Galadima ya bayyana cewa wannan alkalin da ake yada jita-jita a kansa, zai iya zama barazana ga sahihancin sakamakon zaɓukan 2027, inda ya yi gargadin cewa hakan na iya jefa Najeriya cikin rikici.

Google search engine

Galadima ya kuma zargi gwamnatin Tinubu da rashin mutunta dokar ƙasa, inda ya ce tuni an riga an lalata sahihancin INEC domin fifita jam’iyyar APC.

Ya yi nuni da cewa an taɓa naɗa wani da ya rike muƙamin sakatare a jam’iyyar APC kuma ya yi aiki a kotu, daga bisani aka ba shi shugabancin INEC.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara