Manoma da masu sarrafa shinkafa a Najeriya sun soki manufofin gwamnatin tarayya bayan da alkaluma suka nuna cewa yawan kudaden shigo da kayayyakin gona ya kai Naira tiriliyan 2.22 cikin watanni shidan farko na shekarar 2025.
Rahoton jaridar Punch ya ce, a kwanakin baya ma, Shugaba Bola Tinubu ya bayar da umarni ga kwamitin majalisar zartarwa na tarayya da ya tabbatar da saukar farashin abinci a duk fadin kasar.
Karamin ministan noma da tsaron abinci, Sabi Abdullahi, ne ya bayyana hakan a Abuja yayin taron horas da manema labarai na majalisar dattawa.
Sai dai wannan umarni ya gamu da suka daga manoma da masu sarrafa shinkafa, wadanda suka ce tsarin cinikayyar kayan amfanin gona zai fada cikin rudani, maimakon daidaita shi.
Ya kara da cewa mafi dacewa shi ne gwamnati ta kira manyan masu ruwa da tsaki a harkar noma da sufuri, a tattauna da su tare da samar da tallafi kafin bayar da irin wannan umarni.



