DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Matsalar tsaron Katsina ta ragu da kaso 70 – Gwamnatin jihar

-

Gwamnatin Katsina ta ce an samu raguwar ayyukan ta’addanci da kaso 70 a fadin jihar, biyo bayan daukar muhimman matakai wajen kawo karshen matsalar tsaron da ke addabar sassan ta.

Kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida na jihar Dr. Nasir Mu’azu ne ya bayyana haka yayin wani muhimmin taron bayar da rahoton halin da ake ciki kan tsaro, wanda gwamna Dikko Umaru Radda ya shirya.

Google search engine

Wata sanarwa da fadar gwamnatin jihar ta fitar, ta bayyana cewa irin matakan da gwamnatin ke dauka ya sanya da yawa daga cikin jagororin ‘yan bindiga ajiye makamansu tare da neman a yi sulhu.

Sanarwar ta kuma ce jagororin al’umma na ci gaba da yunkurin daukar gabaren yin sulhu da’ yan bindiga a wasu karin yankunan jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara