Jigo a jam’iyyar NNPP a Najeriya Buba Galadima, ya zargi gwamnatin shugaba Tinubu da yunkurin kaucewa gudanar da sahihin zabe a shekarar 2027.
Buba Galadima ya bayyana haka ne a gidan talabijin na Arise, inda ya yi zargin cewa gwamnatin Tinubu ta sanya gwamnatocin jihohi a karkashin ikonta, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.
A cewar sa, gwamnatin na taka rawa wajen kawo hargitsi a cikin jam’iyyun hamayya, tare da cewa ya jiyo rade-radin shugaba Tinubu zai sauya shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta Najeriya INEC, inda ya yi gargadi kan hakan.
A bangare guda, ya soki hukumar ta INEC kan yadda ya ce ta gaza daukar mataki kan masu gudanar da yakin neman zabe tun kafin lokacin da doka ta tanada.



