DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tinubu bai shirya gudanar da sahihin zabe a 2027 ba – Buba Galadima

-

Jigo a jam’iyyar NNPP a Najeriya Buba Galadima, ya zargi gwamnatin shugaba Tinubu da yunkurin kaucewa gudanar da sahihin zabe a shekarar 2027.

Buba Galadima ya bayyana haka ne a gidan talabijin na Arise, inda ya yi zargin cewa gwamnatin Tinubu ta sanya gwamnatocin jihohi a karkashin ikonta, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

Google search engine

A cewar sa, gwamnatin na taka rawa wajen kawo hargitsi a cikin jam’iyyun hamayya, tare da cewa ya jiyo rade-radin shugaba Tinubu zai sauya shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta Najeriya INEC, inda ya yi gargadi kan hakan.

A bangare guda, ya soki hukumar ta INEC kan yadda ya ce ta gaza daukar mataki kan masu gudanar da yakin neman zabe tun kafin lokacin da doka ta tanada.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara