Mataimakin shugaban Nijeriya Kashim Shettima na jagorantar taron majalisar tattalin arzikin kasar a Abuja.
Wannan shi ne karon farko da ake gudanar da taron, tun bayan zaman da shugaba Tinubu ya jagoranta kan batun kirkirar ‘yan sandan jihohi, kamar yadda jaridar punch ta ruwaito.
Taron dai wanda aka fara shi da misalin karfe 11:30 na safiyar Alhamis, ya kunshi gwamnonin Najeriya, gwamnan babban bankin kasar da kuma wasu ministoci domin samarwa da tattalin arzikin kasar ingantacciyar makoma.



