DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ruwan sama mai karfi ya yi ajalin mutum 3, tare da shafe gidaje 1,415 a Adamawa

-

Hukumar ba da agajin gaggawa ta ƙasa NEMA ta tabbatar da cewa mutum uku sun rasa rayukansu, yayin da gidaje sama da 1,415 suka shiga halin tsaka mai wuya sakamakon ambaliyar ruwa da ta biyo bayan ruwan sama a Jihar Adamawa.

Lamarin ya auku ne a ranar Talata a ƙananan hukumomin Yola ta Arewa da Yola ta Kudu.

Google search engine

Rahoton hukumar ya nuna cewa mutane sama da 40 sun jikkata, yayin da gonaki da muhimman gine-gine suka cika da ruwa, lamarin da ya tilasta wa daruruwan iyalai kauracewa gidajensu.

Hukumar ta ce bincike gaggawa da ofishin ta na Yola ya gudanar tare da haɗin gwiwar hukumar ADSEMA da sauran masu ruwa da tsaki ya gano cewa ƙauyuka 13 ne abin ya shafa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara