Hukumar kula da shige da fice ta Sweden ta ce ‘yan Najeriya sama da 7,646 ne suka nemi mafaka a kasar cikin shekaru 24.
Wasu bayanai da jaridar Punch ta tattaro daga shafin yanar gizo na hukumar, sun nuna cewa a tsawon wannan lokaci, ‘yan Najeriya na ci gaba da tururuwar neman mafaka a kasar.
Kazalika bayanan sun nuna cewa a nahiyar Afirka, Najeriya na cikin jerin kasashe 5 da al’ummarta suka fi yawan neman mafaka a kasar.
Sudan, Somalia, Eritrea da kuma Ethiopia su ne kan gaba sakamakon ta’azzarar matsalolin tsaro da na tattalin arziki.



