Jam’iyyar adawa ta PDP a Najeriya ta ce shugaba Bola Tinubu ya fara shirye-shiryen mika mata ragamar mulki domin kuwa ‘yan kasar ba za su sake zabar sa ba.
Yayin tattaunawa da jaridar Punch a sakatariyar jam’iyyar da ke Yola, sakataren tsare-tsaren PDP a jihar Adamawa Hamza Madagali, ya ce ‘yan Najeriya ba su da karfin sake jure irin shugabancin gwamnatin APC a 2027.
A cewar sa, tsare-tsaren da gwamnatin APC ke bullo da su ba su yi daidai da al’umma da kuma tattalin arzikin Najeriya ba.
Ya kara da cewa a halin yanzu’ yan Najeriya sun kara wayo, saboda haka ba za su yadda su salwantar da makomar ‘ya’yansu ba.



