DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Majalisar Dattawa ta sake bude Ofishin Sanata Natasha da aka rufe a baya

-

Majalisar Dattawan Nijeriya ta buɗe ofishin Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, mai wakiltar Kogi ta Tsakiya, wanda aka rufe tsawon watanni shida sakamakon dakatar da ita.

Rahotanni sun nuna cewa ofishin nata da ke a ginin majalisar dattawa an buɗe shi ne a ranar Talatar nan.

Google search engine

Wannan na iya zama alamar cewa za ta dawo bakin aiki, yayin da majalisar ke komawa daga hutun da take a ranar 7 ga Oktoba, 2025.

A makon da ya gabata, Sanata Natasha ta rubuta wa shugabancin majalisar dattawa wasiƙa, inda ta sanar da niyyarta ta komawa bakin aiki bayan shafe tsawon watanni shida bisa dakatarwar da aka yi mata.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara