Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da Sakataren Majalisar Kamoru Ogunlana, ya fitar a ranar Talata a Abuja, inda ya ce jinkirin ya zo ne bisa umarnin shugabannin majalisar dattawa da ta wakilai.
Sakataren ya bayyana cewa, duk da jinkirin komawar zauren majalisar, kwamitoci za su ci gaba da gudanar da ayyukansu a wannan lokaci.
Ya kuma nemi ’yan majalisa da su daidaita jadawalin ayyukansu bisa sabon lokacin tare da bada haƙuri kan duk wata matsala da hakan ka iya haifarwa.
Tun daga ranar 23 ga Yuli, 2025, majalisar ta shiga hutu na shekara, inda aka tsara a dawowarta a watan ranar 7ga watan Satumba domin Ci gaba da aiyukan majalisar.



