DCL Hausa Radio
Kaitsaye

ASUU ta bai wa gwamnatin Najeriya wa’adin makonni biyu

-

Kungiyar malaman jami’o’i ta Najeriya ASUU ta bai wa gwamnatin tarayya wa’adin makonni biyu don biya mata bukatunta.

Kungiyar ta dauki matakin ne biyo bayan wani taron majalisar zartaswa da ta gudanar a Abuja, kamar yadda jaridar punch ta ruwaito.

Google search engine

Wata sanarwa da shugaban kungiyar Farfesa Chris Piwuna ya sanya wa hannu, ta koka da yadda ta ce gwamnatin na yawan yin watsi da al’amuran da suka shafi kungiyar, da ma sauran harkokin jami’o’i a Najeriya.

A cewar sa, muddin wa’adin ya kare gwamnati ba ta dauki matakin da ya dace ba, babu wani zabi da ya wuce ta tsunduma yajin aikin gargadi na makonni biyu, daga nan kuma ta fara na sai baba ta gani.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara