DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Taron sulhunta PENGASSAN da matatar Dangote ya koma ofishin NSA

-

Gidan Talabijin na Channels ya ruwaito cewa taron sulhu tsakanin shugabannin ƙungiyar ma’aikatan PENGASSAN da kuma jagorancin matatar man fetur ta Dangote an mayar da shi zuwa ofishin mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro NSA.

Rikicin ya samo asali ne daga matsalolin kwadago da ba a warware ba tsakanin ɓangarorin biyu.

Google search engine

Ministan kwadago da ayyukan yi, Mohammed Dingyadi, tare da wasu daga cikin shugabannin PENGASSAN da suka isa wurin taron tun farko, sun bar wajen inda suka nufi ofishin NSA inda ake gudanar da tattaunawar.

Yanzu haka dai taron na gudana ne a cikin sirri, kamar yadda rahotanni suka bayyana

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara