DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Najeriya ta fara farautar wadanda wa’adin bizarsu ya kare a kasar

-

Hukumar kula da shige da fice ta Najeriya ta bayyana cewa daga yau 1 ga watan Oktoba za ta fara farautar wadanda wa’adin bizarsu ya kare, kuma su ke ci gaba da zama a kasar, ba tare da yin abin da ya dace ba.

Kafin wannan lokaci dai gwamnatin Najeriya ta bayar da kariya na tsawon watanni uku ga wadanda wa’adin bizar ta su ya kare.

Google search engine

Wata sanarwa da mai magana da yawun hukumar Akinsola Akinlabi ta fitar, ta bayyana cewa farautar za ta mayar da hankali wajen zakulo ‘yan Ć™asashen waje da suka karya dokar zama a Najeriya, kamar yadda The Nation ta ruwaito.

Kazalika ta ce hukuncin da za a dauka kan wadanda aka kama, ya hadar da biyan tara, mayar da su ainahin kasashensu har ma da haramta shigowa Najeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara