DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Nijeriya na bukatar shugabanni masu gaskiya don samar da sauyi mai kyau – Sanata Natasha

-

Sanata mai wakiltar Kogi ta tsakiya Natasha Akpoti Uduaghan ta bayyana damuwa da cewa, Nijeriya ba za ta samu sauyi na gaske ba har sai an samu nagartaccen shugabanci.

Natasha ta fadi haka ne a sakonta na murnar cikar Nijeriya shekaru 65 da samun ‘yancin kai.

Google search engine

A cikin jawabin nata, Uduaghan ta siffanta Nijeriya a matsayin kasa mai fama da matsalolin tsaro, matsin tattalin arziki, rashin daidaito amma duk da haka ta jajirce wajen kirkire-kirkire na basira.

A cewarta, Nijeriyar da magabata suka hango ba kasa ce wadda ta rabu sakamakon kabilanci ko addini ko siyasa ba sai dai wacce adalci, daidaito da arziki ya hada kan al’ummarta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara