Tinubu ya fadi haka ne a ranar Laraba lokacin bikin bude cibiyar al’adu da kirkire-kirkiren fasaha ta Wole Soyinka da aka gyara a Lagos.
Da yake bayani a wajen bikin, shugaba Tinubu ya kara jaddada cewa, wahalhalun da aka sha na matsin tattalin arziki ya wuce.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito Tinubu ya kuma roki yan ‘yan Nijeriya da su yarda da kansu tare da fadin alheri a kan Nijeriya ba akasin hakan ba.



