DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Soke faretin bikin ranar ‘yancin kai ya bani damar sharara barci a ranar, in ji Tinubu

-

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa soke faretin bikin cikar kasar shekara 65 da samun ’yanci ya ba shi damar yin barci tare da samun natsuwa a ranar bikin.

Tun da fari gwamnatin tarayya ta sanar da soke faretin da aka shirya gudanarwa a ranar Laraba, 1 ga Oktoba 2025, domin bikin ranar ’yancin kai.

Google search engine

Wannan sanarwar ta fito ne daga ofishin Sakataren gwamnatin tarayya, inda aka bayyana cewa daukar matakin ba zai rage muhimmancin wannan rana mai tarihi ba.

A jawabin da ya yi ranar Laraba a wajen kaddamar da cibiyar raya al’adu ta Wole Soyinka a Legas, Tinubu ya ce soke faretin ya ba shi damar samun hutu, yin barci cikin natsuwa tare da samun damar halartar gagarumin bikin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara