Wasu tsofaffin hafsoshin tsaron sun goyi bayan kiran da tsohon hafsan tsaron Nijeriya Janar Lucky Irabor mai ritaya ya yi, na gwamnati ta ayyana dokar ta-baci domin magance ayyukan ta’addanci.
A cikin littafinsa mai taken “Scars: Nigeria’s Journey and The Boko Haram Conundrum” ya bayyana cewa rashin mayar da hankali ne ya kawo nakasu wajen yaki da ayyukan ta’addanci a yankin Arewa Maso Gabashin kasar inda ya bukaci a kafa dokar ta-baci.
Haka kuma ya ce samun goyon bayan majalisar dattawa zai taimaka wajen kawo karshen matsalar ta tsaro.
Janar Lucky Irabor (mai ritaya), wanda ya yi aiki a matsayin Babban Hafsan Tsaron ƙasa a lokacin mulkin tsohon Shugaba Muhammadu Buhari, ya bayyana cewa gwamnatin wancan lokaci ba ta da kayan aikin da za su ba ta damar ayyana dokar ta-baci domin yaƙi kai tsaye da ayyukan ‘yan bindiga a Arewa Maso Gabas.



