Kungiyar dattawa da ta gwamnonin Arewacin Najeriya sun amince da kafa majalisar ci-gaban yankin, wadda za ta taimaka wajen bunkasa tattalin arzikinsa.
Matakin ya biyo bayan rattaba hannu kan yarjejeniyar ci-gaban tattalin arzikin Arewacin Nijeriya a karshen taron zuba hannun jari na masana’antu a yankin da aka kammala a birnin Abuja ranar Litinin.
A cikin sanarwar da aka fitar bayan taron, shugaban taron, Farfesa Ango Abdullahi ya ce, majalisar za ta yi aiki ne karkashin kulawar kungiyoyin biyu domin tabbatar da tsarawa da kuma aiwatar da yadda ci-gaban yankin zai kasance, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.



