Wata matar aure mai suna Zainab Alhassan ta saki mijinta, Tijjani Muhammad, saboda kin gyara wayarta da ta lalace da darajarta ta kai Naira 70,000.
Zainab ta shaida wa kotu cewa ta gaji da zaman auren, don haka tana son ta rabu da mijinta ta hanyar Khul’i – wato irin saki da mace ke maido wa mijinta sadakinta domin ta samu ’yancinta.
Ta ce tana shirye ta mayar da sadaki na N30,000 da ta karɓa domin a sake ta daga auren. Zainab ta bayyana cewa tana kallon fim a wayarta lokacin da mijinta ya fara faɗa da ita, ya kwace wayar ya buga ta a kasa, ta lalace. Sai dai ta ce ba ta da wata shaida da za ta tabbatar da ikirinta.
Shi kuma mijin, Tijjani Muhammad, ya ce bai da matsala da bukatar sakin da matarsa ke nema, amma ya musanta zargin cewa shi ne ya lalata wayar.
Alkali Mu’awiyya Shehu ya raba auren bisa tsarin Khul’i, inda ya amince da sakin amma ya ƙi amincewa da bukatar matar ta biya ta farashin wayar da ta ce mijinta ya lalata.



