DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Wani lauya ya nemi kotu ta hana Jonathan takarar shugabancin Nijeriya a 2027

-

Wani lauya mai suna Johnmary Jideobi ya garzaya babbar kotun Abuja yana neman ta hana tsohon shugaban Najeriya Goodluck Jonathan tsayawa takarar shugaban kasa a zaben 2027.

Jideobi ya kuma nemi kotun da ta hana hukumar zaben Nijeriya amincewa da sunan Jonathan a matsayin dan takara.

Google search engine

A cikin bayanan da ya shigar, ya bayyana cewa, Jonathan ne ya karasa wa’adin mulkin marigayi Umaru Musa ‘Yar’adua daga bisani kuma ya yi shekaru 4 bayan lashe zaben 2011 wanda hakan ya karar da wa’adi biyu da kundin tsarin mulki ya yi masa tanadi, kamar yadda jaridar punch ta ruwaito.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnatin Nijar ta kaddamar da sabon ofishin kamfanin shinkafar gida

Ministan kasuwancin jamhuriyar Nijar, Malam Abdoulaye Seydou ya jagoranci kaddamar da sabon ofishin kamfanin shinkafar gida a babban birnin Yamai a ranar Litinin 13 ga...

Gwamnatin Nijeriya za ta dauki mataki kan barnar kudaden shiga a bangaren hakar ma’adanai

Ministan ma’adanai, Dele Alake, ya bayyana cewa gwamnatin Nijeriya na shirin kafa sabuwar hukuma da za ta rika sa ido kan fitar da ma’adanai kafin...

Mafi Shahara