DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaba Tinubu zai karrama mutane 959 da lambar girmamawa ta kasa

-

Shugaban Nijeriya, Bola Tinubu ya amince da karrama mutane 959 da lambar girmamawa ta ƙasa a zaman majalisar kolin kasar da ya wakana a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

Babbar sakatariyar ofishin harkokin ministoci, Dr. Emanso Umobong, ta ce, an zaɓi mutane 824 don karramawar 2024/2025 da kuma wasu 135 na musamman wanda adadin ya kai 959 gaba ɗaya kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

Google search engine

Umobong ta kara da cewa, wadanda aka karrama sun haɗa da fitattun ‘yan Nijeriya da wasu daga ƙasashen waje da suke ba da gudummawa a fannoni daban-daban, ciki har da Bill Gates, tawagar ‘yan kwallon kafa ta mata, Super Falcons, da na kwando, D’Tigress da kuma Farfesa Mahmood Yakubu, shugaban INEC wanda ya sauka daga mukaminsa a cikin kwanakin nan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An gudanar da addu’o’in neman tsari daga hare-haren ‘yan bindiga a jihar Neja

Mazauna yankin jihar Neja ta Arewa sun gudanar da addu’o’i na musamman a filin Idi da ke Kontagora, hedkwatar karamar hukumar Kontagora, domin neman taimakon...

‘Yan siyasa a Nijeriya sun fi maida hanakali kan siyasa maimakon magance matsalolin al’umma – Sarkin Onitsha

Sarkin Onitsha, Igwe Nnaemeka Achebe, ya caccaki ‘yan siyasa bisa mayar da hankali kan siyasa maimakon gudanar da mulki yadda ya kamata tun kafin zaben...

Mafi Shahara