DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tinubu zai halarci taron zuba jarin ’yan Nijeriya mazauna ƙasashen waje a matsayin babban bako

-

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu zai halarci taron zuba jari na ’yan Nijeriya mazauna ƙasashen waje karo na takwas a matsayin bako na musamman, wanda za a gudanar daga ranar 11 zuwa 13 ga watan Nuwamban 2025 a Abuja.

Shugabar hukumar kula da ’yan Nijeriya mazauna ƙetare ‘NiDCOM’ Abike Dabiri-Erewa ce ta sanar da hakan yayin taron manema labarai kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

Google search engine

Abike ta ce tun bayan fara taron a 2018, an samu karuwar zuba jari daga ’yan Nijeriya da ke ƙasashen waje a fannoni kamar gidaje, kiwon lafiya, noma, fasahar sadarwa, makamashi, masana’antu da harkokin kirkire-kirkire.

Dabiri-Erewa ta kara bayyana cewa, a taron bara na 2024 an cimma yarjejeniyar zuba jari da ta kai kimanin naira miliyan 673 a fannoni daban-daban.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An gudanar da addu’o’in neman tsari daga hare-haren ‘yan bindiga a jihar Neja

Mazauna yankin jihar Neja ta Arewa sun gudanar da addu’o’i na musamman a filin Idi da ke Kontagora, hedkwatar karamar hukumar Kontagora, domin neman taimakon...

‘Yan siyasa a Nijeriya sun fi maida hanakali kan siyasa maimakon magance matsalolin al’umma – Sarkin Onitsha

Sarkin Onitsha, Igwe Nnaemeka Achebe, ya caccaki ‘yan siyasa bisa mayar da hankali kan siyasa maimakon gudanar da mulki yadda ya kamata tun kafin zaben...

Mafi Shahara