DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Maryam Sanda na cikin mutane 82 da shugaba Tinubu ya sassauta wa hukunci

-

Iyalan Maryam Sanda, wadda aka yanke wa hukuncin kisa a shekarar 2020 bisa laifin ajalin mijinta, ne suka sake neman gwamnati ta yi mata afuwa bisa hujjar cewa hakan zai kasance maslaha ga ’ya’yanta biyu.

Maryam, mai shekaru 37, ta shafe shekaru shida da watanni takwas a Suleja Medium Security Custodial Centre tun bayan yanke mata hukunci.

Google search engine

Iyalan nata sun bayyana cewa Maryam ta nuna nadama sosai, ta kuma canza salon rayuwarta, inda ta zama misali ga sauran fursunoni saboda kyakkyawan hali da biyayya ga doka a lokacin zaman gidan yari.

A bayanai na baya-bayan nan, da fadar shugaban kasa ta fitar ta hannun Hadimin shugaba Tinubu kan harkokin yada labarai Bayo Onanuga an lura da sunan Maryam a jerin wadanda aka sassautawa hukuncin zuwa daurin rai da rai daga hukuncin kisa na baya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara