DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sojoji sun yi ikirarin juyin mulki a kasar Madagascar

-

Wani sashe na sojin ƙasar Madagascar ya sanar da cewa ya karɓe ikon ƙasar baki ɗaya, abin da shugaban ƙasar Andry Rajoelina ya bayyana a matsayin yunƙurin karɓar mulki ta hanyar da ba ta dace ba.

Jaridar Punch ta rawaito cewa lamarin ya zama sabon salo cikin zanga-zangar da ta yi akalla makonni biyu ana yi a ƙasar saboda matsalolin wutar lantarki da ruwan sha.

Google search engine

A ranar Lahadi, Shugaban kasar Rajoelina ya tabbatar da cewa ana ƙoƙarin yin juyin mulki ta hanyar da ba ta dace ba, yana mai kiran ‘yan ƙasa da su zauna lafiya tare da shiga tattaunawa domin warware rikicin da ke addabar ƙasar.

Rahotanni sun nuna cewa akalla mutane 22 ne suka rasa rayukansu tun bayan barkewar zanga-zangar a ranar 25 ga Satumba, sakamakon harbin jami’an tsaro.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Daga 2026 ₦500,000 kawai ɗan Nijeriya zai iya cira a banki cikin sati ɗaya – CBN

Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya sake fasalin dokokin cire kuɗi daga bankuna kan sabon tsarin da zai fara aiki daga watan Janairun 2026. Babban bankin ya...

Ƴan kwangila sun girke akwatin gawa a ofishin ma’aikatar kuɗin Nijeriya

‘Yan kwangila sun girke akwatin gawa a kofar shiga ofishin ma’aikatar kudin Nijeriya da ke Abuja.   ‘Yan kwangilar, karkashin inuwar kungiyarsu ta 'yan asalin Nijeriya sun...

Mafi Shahara