DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sarkin Musulmi ya bukaci gwamnati da ta yi doka kan amfani da kafafen sada zumunta

-

Sarkin Musulmi Alhaji Sa’ad Abubakar III ya bukaci gwamnati da ta yi doka domin daidaita amfani da kafafen sada zumunta a Nijeriya saboda yadda ake amfani da su wajen yada maganganu marasa ladabi da suke haddasa fitina.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa Sarkin ya bayyana hakan ne ta bakin Sarkin Zazzau, Ambasada Ahmad Nuhu Bamalli, yayin taron koli na malaman Arewa kan matsalar tsaro da tattalin arziki da kungiyar malaman Arewa ta shirya a Kaduna.

Google search engine

Ya ce rashin kula da kafafen sada zumunta na iya jefa kasar cikin tashin hankali da rikice-rikicen kabilanci da addini.

A cewarsa, yanzu kowa na iya zagin shugaba, malami ko mutane masu kima da mutunci ba tare da hukunci ba.

A wasu ƙasashe ana bin diddigin duk wanda ya yada kalaman da ke tada fitina, ana kuma hukunta shi, kamata ya yi a yi irin haka a Nijeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisar Dattawa ta tabbatar da Farfesa Amupitan a matsayin shugaban hukumar zaben Nijeriya INEC

Majalisar Dattawan Nijeriya ta tabbatar da nadin Farfesa Joash Amupitan a matsayin sabon shugaban hukumar zaben Nijeriya INEC. Jaridar Punch ta ruwaito cewa majalisar ta amince...

Jam’iyyar ADC ta zargi shugaba Tinubu da son maida Nijeriya amfani da jam’iyya guda

Jam’iyyar ADC ta zargi shugaba Bola Ahmed Tinubu da ƙoƙarin juya Nijeriya zuwa kasa mai amfani da jam’iyya ɗaya, bayan ficewar wasu gwamnonin jihohi daga...

Mafi Shahara