DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Nijeriya ta ce cin jarabawar lissafi “Mathematics” wajibi ne ga daliban Sakandare kafin kammalawa

-

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa lallai dukkan ɗalibai masu rubuta jarabawar kammala sakandare su cigaba da rubuta lissafi tare da harshen Turanci a matsayin wajibi.

Mai magana da yawun ma’aikatar ilimi ta Nijeriya Boriowo Folashade ce ta bayyana hakan cikin wata sanarwa a Lahadinan.

Google search engine

A ranar Talata Boriowo ta sanar da cewa ɗaliban sashen fasaha da zamantakewa ba za a sake buƙatar lallai sai sun samu kiredit a lissafi ba kafin su samu gurbin karatu a jami’a ko kwalejin kimiyya sanarwar da ta jawo ce-ce-ku-ce tsakanin masana ilimi da jama’a.

Sai dai a sabon bayanin ta ce wannan gyara bai soke wajabcin ɗalibai su rubuta jarabawar lissafi da Turanci ba, illa dai ya ba jami’o’i damar karɓar ɗalibai zuwa wasu fannoni ko shirye-shiryen karatu da ba lissafi ko Turanci ke zama tilas ba.

A cewarta, wannan mataki na cikin shirin gwamnati na tabbatar da daidaito da ba kowa dama wajen samun ilimi, tare da bunƙasar ci-gaban ɗan Adam kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Fadar Shugaba Tinubu ta soki Atiku kan kwatanta gwamnatinsa da ta mulkin soja

Fadar Shugaban Nijeriya ta caccaki madugun adawa Atiku Abubakar, bisa kwatanta gwamnatin Tinubu da mulkin soja, tana mai bayyana kalaman nasa a matsayin abinda basu...

Majalisar Dattawa ta dakatar da muhawara kan gyaran dokar zabe tare da shiga zaman sirri

Majalisar Dattawan Nijeriya ta dakatar da muhawarar kan kudirin dokar zaɓe ta 2022, domin bai wa ’yan majalisa damar yin nazari mai zurfi kafin ɗaukar...

Mafi Shahara