DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Nijeriya ta ce cin jarabawar lissafi “Mathematics” wajibi ne ga daliban Sakandare kafin kammalawa

-

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa lallai dukkan ɗalibai masu rubuta jarabawar kammala sakandare su cigaba da rubuta lissafi tare da harshen Turanci a matsayin wajibi.

Mai magana da yawun ma’aikatar ilimi ta Nijeriya Boriowo Folashade ce ta bayyana hakan cikin wata sanarwa a Lahadinan.

Google search engine

A ranar Talata Boriowo ta sanar da cewa ɗaliban sashen fasaha da zamantakewa ba za a sake buƙatar lallai sai sun samu kiredit a lissafi ba kafin su samu gurbin karatu a jami’a ko kwalejin kimiyya sanarwar da ta jawo ce-ce-ku-ce tsakanin masana ilimi da jama’a.

Sai dai a sabon bayanin ta ce wannan gyara bai soke wajabcin ɗalibai su rubuta jarabawar lissafi da Turanci ba, illa dai ya ba jami’o’i damar karɓar ɗalibai zuwa wasu fannoni ko shirye-shiryen karatu da ba lissafi ko Turanci ke zama tilas ba.

A cewarta, wannan mataki na cikin shirin gwamnati na tabbatar da daidaito da ba kowa dama wajen samun ilimi, tare da bunƙasar ci-gaban ɗan Adam kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Daga 2026 ₦500,000 kawai ɗan Nijeriya zai iya cira a banki cikin sati ɗaya – CBN

Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya sake fasalin dokokin cire kuɗi daga bankuna kan sabon tsarin da zai fara aiki daga watan Janairun 2026. Babban bankin ya...

Ƴan kwangila sun girke akwatin gawa a ofishin ma’aikatar kuɗin Nijeriya

‘Yan kwangila sun girke akwatin gawa a kofar shiga ofishin ma’aikatar kudin Nijeriya da ke Abuja.   ‘Yan kwangilar, karkashin inuwar kungiyarsu ta 'yan asalin Nijeriya sun...

Mafi Shahara