DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tinubu ya gargadi Alkalan Nijeriya da kada su karkata ga cin hanci ko rashin adalci

-

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi kira ga alkalai da sauran ma’aikatan shari’a a Najeriya da su ci gaba da zama masu gaskiya, adalci, da rashin cin hanci wajen aiwatar da shari’a.

Tinubu ya gargadi cewa rushewar kowace al’umma yana farawa ne idan masu fassara dokokinta suka zama masu karkata ko cin hanci.

Google search engine

Yayin bude taron bita na hukumar EFCC tare da Cibiyar Alƙalai ta Ƙasa (NJI) a birnin Abuja ranar Litinin, wanda mataimakinsa, Kashim Shettima, ya wakilce shi, Shugaba Tinubu ya ce ginshiƙin ɗabi’ar Najeriya yana ta’allaka ne da amincin tsarin shari’arta.

Ya ce gwamnatin sa tana ƙoƙarin inganta walwala da yanayin aiki na ma’aikatan shari’a, inda sabbin karin albashi da aka yi kwanan nan ke cikin matakan da ake ɗauka don ƙarfafa ikon shari’a mai zaman kanta.

Premium Times ta ruwaito Shugaban ya kuma tabo batun jinkirin shari’a a manyan shari’o’in cin hanci da rashawa, yana mai cewa akwai buƙatar inganta saurin yanke hukunci kamar yadda ake yi a shari’o’in zamba ta yanar gizo.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

PDP ta musanta zargin kirƙirar sa hannun Sakataren ta na kasa

Kwamitin zartaswa na Ƙasa na jam’iyyar PDP ya musanta zargin ƙirƙirar sa hannu da Sakataren jam’iyyar na ƙasa, Sanata Samuel Anyanwu, ya yi. Mai magana da...

‘Yan sanda sun kama barawon da ya yi amfani da kakin NYSC don yi fashi a Enugu

Rundunar ‘Yan Sanda ta Jihar Enugu ta kama wani mutum da ake zargi da yin fashi da makami, ta hanyar basaja da kakin NYSC domin...

Mafi Shahara