DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Hukumomi za su sake bibiyar wadanda Tinubu ya yi wa afuwa don tantance su

-

Gwamnatin Nijeriya ta ce rundunar ‘yansanda, hukumar yaki da yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa ta EFCC, tare da NDLEA mai yaki da sha da fatauci miyagun ƙwayoyi ne za su sake bibiyar jerin mutanen da shugaba Tinubu ya yi wa afuwa don tantance su.

 

Google search engine

Jaridar Punch ta ruwaito ministan shari’a na Nijeriya Lateef Fagbemi SAN na cewa daukar matakin wani yunkuri ne na tabbatar da gaskia da adalci a kan batun afuwar.

Labari mai alaka: Gwamnati Nijeriya tace haryanzu ba a saki kowa ba a cikin mutanen da Tinubu ya yiwa afuwa

Haka kuma shugaba Tinubu na jiran sakamakon da wadannan hukumomi za su fitar, don daukar matakan da suka dace.

Labari mai alaka: Ni na roki gwamnati da ta yafe ma Maryam Sanda – Mahaifin Bilyaminu Bello

Sai dai jaridar ta yi hasashen cewa akwai yiwuwar a cire fiye da rabin sunayen wadanda aka yi wa afuwar da zarar an kammala binciken.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon Minista Tanimu Turaki ya zama ɗan takarar shugabancin jam’iyyar PDP na Arewa

Jagororin jam’iyyar PDP na yankin Arewacin Nijeriya sun amince da tsohon Ministan Harkoki. A Musamman, Tanimu Turaki (SAN), a matsayin ɗan takarar da suka amince...

Jam’iyyar ADC a Kaduna ta kori mataimakin shugabanta da wasu ‘ya’yanta 8

Jam'iyyar hadaka ta ADC mai hamayya a Nijeriya reshen Kaduna ta kori mataimakin shugabanta na jihar tare da wasu manyan jami'anta guda takwas, bayan samun...

Mafi Shahara