DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jonathan na kara fuskantar matsin lamba domin janye kudirin tsayawarsa takarar shugaban kasa a 2027

-

Tsohon shugaban ƙasa Goodluck Jonathan na fuskantar matsin lamba daga manyan jiga-jigai na yankin Niger Delta da ke ƙoƙarin ganin ya janye kudirin sake neman kujerar shugaban ƙasa a zaben 2027, tare da mara wa Shugaba Bola Tinubu baya don tazarcensa.

Rahoton jaridar Punch ya bayyana cewa tsohon jagoran ‘yan tawaye, Government Ekpemupolo, wanda aka fi sani da Tompolo, ne ke jagorantar wannan yunkuri na shawo kan Jonathan ya janye aniyarsa, tare da goya ma shugaba Tinubu baya a wa’adinsa na biyu.

Google search engine

Tompolo tare da abokansa da suka haɗa da shugaban Tantita Security Services Nigeria Limited, Kestin Pondi, da mataimakin dan takarar gwamnan APC a Bayelsa a 2023, Joshua Maciver, sun kai ziyarar sirri ga Jonathan a gidansa da ke Otuoke, ƙaramar hukumar Ogbia, ranar 16 ga watan Oktoba, 2025.

Rahotanni sun ce taron ya ɗauki sa’o’i da dama, wanda ya nuna muhimmancin batun.

Majiyoyi daga kusa da bangarorin biyu sun tabbatar da cewa ziyarar ba ta da nasaba da batun tsaro kamar yadda aka ruwaito a baya, illa dai tattaunawa ce ta siyasa da nufin ganin Jonathan ya mara wa Tinubu baya a zaben 2027.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Ka fito ka bayyana wa ‘yan Nijeriya hakikanin dalilin da ya sa ka canza hafsoshin tsaro – Bukatar ADC ga shugaba Tinubu

Jam’iyyar ADC ta bukaci shugaban Nijeriya, Bola Tinubu ya bayyana gaskiya ga ’yan Nijeriya kan ainihin dalilan da suka sa aka yi gaggawar sauya shugabannin...

Gwamnan jihar Bauchi Bala Muhammad ya nada yayansa a matsayin Sarkin Duguri

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, ya naɗa yayansa, Alhaji Adamu Mohammed, a matsayin sarkin sabon masarautar Duguri da aka ƙirƙira a jihar. Sakataren gwamnatin Jiha, Aminu...

Mafi Shahara