DCL Hausa Radio
Kaitsaye

PDP ta dage tantance ‘yan takara na babban taronta na kasa

-

Dagewar ta zo ne ’yan sa’o’i bayan tsohon gwamnan Jihar Jigawa, Alhaji Sule Lamido, ya ayyana shirinsa na takarar shugabancin jam’iyyar, duk da cewa wasu ’yan yankin Arewa maso Yamma na jam’iyyar sun riga sun amince da tsohon minista Kabiru Tanimu Turaki (SAN) a matsayin ɗan takarar da aka amince da shi.

Kodayake, wasu bangarori na PDP, ciki har da masu goyon bayan Lamido da Nyesom Wike, sun ƙi amincewa da wannan yarjejeniya, lamarin da ke nuna rikici da rarrabuwar kai a cikin jam’iyyar a daidai lokacin da muhimman mambobi ke ficewa.

Google search engine

Shugaban Kwamitin Shirya Taron Gangamin Kasa kuma Gwamnan Jihar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri, ne ya sanar da hakan a wata takarda da ya fitar a ranar Litinin, inda ya ce wasu dalilai ne na ba-zata suka sa aka jinkirta taron.

Fintiri ya bayyana cewa za’a sanar da sabuwar ranar taron a nan gaba, ya kuma tabbatar da cewa kwamitinsu na da cikakken kudiri na gudanar da taron gangami cikin gaskiya da lumana.

Rahoton jaridar Punch ya ce ana sa ran PDP za ta gudanar da taron gangamin zabenta tsakanin 15 zuwa 16 ga Nuwamba, 2025 a Ibadan, Jihar Oyo.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara