DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Hukumar agajin gaggawa NEMA ta karɓi ƴan Nijeriya 153 da suka makale a Chadi

-

Hukumar ba da agajin gaggawa ta Nijeriya NEMA, ta bayyana cewa ta karɓi ’yan Nijeriya 153 da suka dawo daga ƙasar Chadi, ƙarƙashin shirin Ƙungiyar Kula da Ƴan Gudun Hijira ta Duniya (IOM) tare da haɗin gwiwar Gwamnatin Tarayya.

Kamar yadda sanarwar ofishin NEMA na Legas ta nuna a shafin X ranar Talata, matafiyan sun iso filin jirgin saman Murtala Muhammed da ke Legas a ranar Lahadi, 27 ga Oktoba, 2025, da misalin ƙarfe 12:15 na rana, ta jirgin ASKY Airlines mai lamba CAS-AC.

Google search engine

Sanarwar ta ce cikin matafiyan da suka dawo akwai manya 105 (maza 63 da mata 42), yara 45 (maza 25 da mata 20), da jarirai 3, dukkaninsu mata.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisar wakilan Nijeriya ta amince wa Tinubu ya ciyo bashin dala biliyan 2.35

Majalisar wakilai ta Nijeriya ta amince da bukatar shugaban Tinubu na neman bashin dala biliyan 2.347 daga ƙasashen waje domin cike gibin kasafin kuɗin 2025...

Sojojin Nijeriya za su murƙushe ‘yan ta’addan Lakurawa — Babban hafsan sojin kasa Janar Waidi Shaibu

Babban hafsan sojin kasa, Manjo Janar Waidi Shaibu, ya sha alwashin murƙushe sabuwar ƙungiyar ‘yan ta’addan Lakurawa wadda ke addabar wasu sassan arewacin Nijeriya. Janar Shaibu,...

Mafi Shahara