DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ciyo bashi bayan cire tallafin man fetur ba dai-dai bane – Sarki Muhammadu Sanusi II

-

Tsohon gwamnan babban bankin Nijeriya CBN kuma Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, ya soki gwamnati bisa ci gaba da ciyo bashi duk da cire tallafin man fetur.

Sarki Sanusi ya bayyana haka ne a ranar Talata yayin wani taro da aka gudanar a Abuja, inda ya ce cire tallafin man ya karawa gwamnati kuɗaɗen shiga, don haka bai dace a ci gaba da aro kudi ba.

Google search engine

Ya jinjina wa gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu bisa cire tallafi da daidaita farashin musayar kuɗi, yana mai cewa matakan suna da tsauri amma sun zama wajibi.

Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa, Sarkin ya yi gargadin cewa,duk wannan matakan, ba za su yi tasiri ba idan ba’asa gaskiya da tsauraran matakai kan kashe kuɗin gwamnati ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara