Tsohon gwamnan babban bankin Nijeriya CBN kuma Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, ya soki gwamnati bisa ci gaba da ciyo bashi duk da cire tallafin man fetur.
Sarki Sanusi ya bayyana haka ne a ranar Talata yayin wani taro da aka gudanar a Abuja, inda ya ce cire tallafin man ya karawa gwamnati kuɗaɗen shiga, don haka bai dace a ci gaba da aro kudi ba.
Ya jinjina wa gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu bisa cire tallafi da daidaita farashin musayar kuɗi, yana mai cewa matakan suna da tsauri amma sun zama wajibi.
Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa, Sarkin ya yi gargadin cewa,duk wannan matakan, ba za su yi tasiri ba idan ba’asa gaskiya da tsauraran matakai kan kashe kuɗin gwamnati ba.



