DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Majalisar wakilan Nijeriya ta amince wa Tinubu ya ciyo bashin dala biliyan 2.35

-

Majalisar wakilai ta Nijeriya ta amince da bukatar shugaban Tinubu na neman bashin dala biliyan 2.347 daga ƙasashen waje domin cike gibin kasafin kuɗin 2025 da kuma sake biyan wani tsohon bashin a Eurobond.

An amince da bukatar ne bayan rahoton kwamitin Majalisa kan tallafi da harkokin basussuka da shugaban kwamitin, Ɗan majalisa Abubakar Hassan Nalaraba, ya gabatar a zaman majalisar da kakakin majalisar Tajudeen Abbas ya jagoranta.

Google search engine

Jaridar Punch ta rawaito cewa tun bayan da shugaba Tinubu ya hau mulki a watan Mayun 2023, gwamnatinsa ta karɓi basussuka da dama domin tallafa wa shirin gwamnati da ayyukan ci gaba.

A cikin shekaru biyu, Nijeriya ta karɓi sama da dala biliyan 7.2 daga bankin duniya da kuma bashin dala biliyan 1 daga bankin raya Afirka.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara