DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Majalisar wakilan Nijeriya ta amince wa Tinubu ya ciyo bashin dala biliyan 2.35

-

Majalisar wakilai ta Nijeriya ta amince da bukatar shugaban Tinubu na neman bashin dala biliyan 2.347 daga ƙasashen waje domin cike gibin kasafin kuɗin 2025 da kuma sake biyan wani tsohon bashin a Eurobond.

An amince da bukatar ne bayan rahoton kwamitin Majalisa kan tallafi da harkokin basussuka da shugaban kwamitin, Ɗan majalisa Abubakar Hassan Nalaraba, ya gabatar a zaman majalisar da kakakin majalisar Tajudeen Abbas ya jagoranta.

Google search engine

Jaridar Punch ta rawaito cewa tun bayan da shugaba Tinubu ya hau mulki a watan Mayun 2023, gwamnatinsa ta karɓi basussuka da dama domin tallafa wa shirin gwamnati da ayyukan ci gaba.

A cikin shekaru biyu, Nijeriya ta karɓi sama da dala biliyan 7.2 daga bankin duniya da kuma bashin dala biliyan 1 daga bankin raya Afirka.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnatin Tinubu ta fitar da Naira biliyan 2.3 don biyan bashin albashi da karin girma na malaman jami’o’i

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa ta saki kudin da ya kai Naira biliyan 2.3 domin biyan bashin albashi da karin girma na malamai a jami’o’in...

Sojojin Nijeriya za su murƙushe ‘yan ta’addan Lakurawa — Babban hafsan sojin kasa Janar Waidi Shaibu

Babban hafsan sojin kasa, Manjo Janar Waidi Shaibu, ya sha alwashin murƙushe sabuwar ƙungiyar ‘yan ta’addan Lakurawa wadda ke addabar wasu sassan arewacin Nijeriya. Janar Shaibu,...

Mafi Shahara