Shugaban majalisar wakilan Nijeriya Tajudeen Abbas, ne ya sanar da hakan a zaman majalisar da aka yi a Alhamis dinnan, inda ya karanta wasikun sauyin shekar da ‘yan majalisar suka aika masa,wanda Gwamnan Enugu, Barista Peter Mbah, ya halarci zaman.
‘Yan majalisar da suka sauya sheƙa sun ce sun bar jam’iyyunsu ne saboda rikice-rikicen cikin gida da ke addabar jam’iyyun adawa.
Bayan zaɓen 2023, jam’iyyar Labour ce ta lashe kujeru bakwai cikin takwas na jihar Enugu, yayin da PDP ta samu kujera ɗaya.



