DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Nijeriya ta musanta zargin Trump kan kisan Kiristoci a kasar

-

Gwamnatin Nijeriya ta musanta maganganun shugaban Amurka, Donald Trump, da ke cewa ana yawan kisan Kiristoci a Nijeriya tare da kiranta “kasa mai matsalar tauye ‘yancin addini.”

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen Nijeriya, Kimiebi Ebienfa, ya fitar a safiyar Asabar, gwamnatin ta ce wadannan zarge-zargen ba su da tushe kuma ba su bayyana ainihin halin da ake ciki a kasa ba.

Google search engine

Sanarwar ta kara da cewa, karkashin shugabancin Bola Ahmed Tinubu, Nijeriya na ci gaba da yaki da ta’addanci tare da karfafa zaman lafiya da fahimtar juna tsakanin addinai, da kuma kare rayuka da hakkin ‘yan kasa kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

Hakazalika, sanarwa ta ce gwamnatin Nijeriya za ta cigaba da tattaunawa da gwamnatin Amurka domin kara fahimtar juna kan kokarin da ake yi wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaro a yankin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara